Tattaunawa Da Ra'ayin Masu Saurare

Ra'ayoyin masu saurare kan matakin IPOB na shiga tattaunawa da Najeriya

Informações:

Sinopsis

Jagoran IPOB da ke fafutukar kafa ƙasar Biafra a Najeriya Nnamdi Kanu, ya ce a shirye yake ya shiga tattaunawa da gwamnati domin kawo ƙarshen kai-da-kawon da ake yi da shi a gaban kotu. Kanu, wanda mahukuntan ƙasar Kenya suka kama tare da miƙa wa Najeriya shi tun a 2021, yanzu haka yana fuskantar tuhume-tuhume ciki har da na ta’addanci da kuma cin amanar ƙasar.Shin ko tattaunawa ita ce mafita don warware wannan al’amari?Ko wataƙila sakin Nnamdi Kanu zai iya taimakawa domin samar da zaman lafiya musamman a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya?Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Ayeeshat Jibrin Ahmed