Al'adun Gargajiya

  • Autor: Vários
  • Narrador: Vários
  • Editor: Podcast
  • Duración: 3:59:52
  • Mas informaciones

Informações:

Sinopsis

Kawo aladu na zamani da wadanda suka shude daga sassan kasashen duniya domin mai sauraro ya san cewa, duniyarmu tana da girma da yawan jamaa masu aladu daban-dabam.  Akwai kuma Shirin al'adunmu na musamman na karshen mako da mu ke gabatarwa a ranakun Asabar da lahadi.

Episodios

  • Shin wa yafi buwaya da kuma kwarewa a waƙa tsakanin Shata da Rarara

    20/05/2025 Duración: 10min

    Shirin al'adun mu na Gado na wannan mako zai Dora kan ci gaban Muhawara a tsakanin Masana kan kwarewar waƙa a tsakanin mawaki Shata da kuma Rarara Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin, tare a Nasiru Sani

  • Muhawwara akan bambamci da kamanceceniya tsakanin Shata da Rarara

    13/05/2025 Duración: 09min

    Shirin al’adu na wannan makon ya waiwayi al’adar waƙoƙin Hausa ne da kuma tasirin Mawaƙan da suke rera su waƙoƙin a fannonin rayuwa daban daban.  A baya bayan nan aka tafka muhawara tsakanin wasu masana guda biyu na Adabin Hausa wato Dakta Abdul-Shakur Yusuf Ishaq na Jami’ar Jihar Kaduna da kuma Dakta Mu’azu Sa’adu Kudan na Jami’ar Sule Lamiɗo da ke Kafin Hausa a jihar Jigawa, waɗanda suka baje iliminsu a kan matakin shahara, da kamance-ceniya da kuma banbanci a tsakanin Marigayi Mamman Ibrahim Yero da aka fi sani da Mamman Shata ko kuma Shata mai Ganga  da kuma Dauda Adamu Kahutu Rarara da a halin yanzu zamani ke tafiya da shi.

  • Yadda camfi ke shafar rayuwar al'umma a wannan lokaci

    06/05/2025 Duración: 10min

    Shirin a wannan makon zai tattauna ne a kan Camfi, da kuma yadda ya kasance a zamanin kaka da kakanni, da rawar da ya taka a waccan lokaci da kuma yadda yake shafar rayuwar jama’a a lokacin da muke.Duk da ƙarancin lokaci, shirin Al’adunmu na gado zai yi ƙoƙarin zayyana rabe-raben al’adar ta Camfi ko kuma wasu daga ciki.

  • Tasirin suturar ƙabilar Dagomba da ke ci gaba da mamaye sassan Ghana

    29/04/2025 Duración: 10min

    Shirin al'adunmu na gado tare da Oumarou Sani a wannan mako ya mayar da hankali ne kan al'adun ƙabilar Dagomba a ƙasar Ghana, ƙabilar da ke ci gaba da mamaya a wannan ƙasa ta yammacin Afirka suk da kasancewarta wadda a baya tafi ƙarfi a yankin arewacin ƙasar. Yanayin suturun wannan ƙabila na daga cikin abin da ke jan hankalin jama'a, musamman yanayin hularsu wadda ke da nufin ko kuma ma'anar zaman lafiya.Suturun wannan ƙabila dai akan saƙa su da hannu ne.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

página 2 de 2