Wasanni

Informações:

Sinopsis

A kowace Litinin da Juma'a a shirye-shiryen Safe da Dare ana gabatar da Shirin Duniyar Wasanni akan batutuwa daban-daban da suka shafi wasanni a sassan duniya.

Episodios

  • Yadda kasashe ke bayar da mamaki a wasannin gasar AFCON a Ivory Coast

    22/01/2024 Duración: 09min

    Shirin duniyar wasanni tare da Khamis Saleh ya mayar da hankali kan yadda gasar AFCON ke ci gaba da gudana a Ivory Coast, gasar da zuwa yanzu aka kammala zagaye biyu na matakin rukuni. Gasar ta AFCON a bana ta zo da wani yanayi ta yadda kasashen da ba a tsammanin su iya kai labari ke ci gaba da bayar da mamaki, yayinda wasu manyan kasashe kuma a fagen tamaular nahiyar suka kasa katabus.Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin..

  • Yadda aka kammala wasannin farko na rukuni a gasar AFCON

    19/01/2024 Duración: 09min

    Shirin "Duniyar Wasanni" a wannan lokaci zayyi duba ne akan yadda aka kammala wasannin farko na matakin rukuni da kuma yadda aka faro na biyu a gasar AFCON da ke gudana a Ivory Coast. An kuma fara wasannin ne da karawar da aka yi tsakanin Equatorial Guinea Guinea-Bissau, inda Equatorial Guinea ta samu nasara akan Guinea-Bissau da ci 4-2. Sai kuma wasa na biyu da aka yi a rukunin na A tsakanin Najeriya da Ivory Coast mai masaukin baki, kuma kwallo daya mai ban haushi da zura tawagar Super Eagles ta Najeriya ta zura ta hannun William Troost-Ekong ce ta bada nasara a wasan.Wannan nasara ta farko da Super Eagles ta samu a rukunin A, ta farfado da fatan Najeriya na kai wa zagaye na biyu a gasar lashe kofin Afrika, yayinda ita kuwa Ivory Coast hannun agogo ya koma mata baya.Ku lastsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......

  • Gasar cin kofin kasashen Afirka ta kankama a Ivory Coast

    15/01/2024 Duración: 09min

    A ranar asabar da ta gabata ne aka fara gasar lashe kofin nahiyar Afrika wato AFCON da kasar Ivory Coast ke karbar bakunci. Wannan ne karo na 34 da ake gudanar da wannan gasa, kuma kasashe 24 zasu fafata a matakin rukuni.

  • Yadda aka daina bai wa matasan 'yan wasan Najeriya dama a Super Eagles

    29/12/2023 Duración: 09min

    Shirin a wannan mako ya mayar da hankali ne ga batun yadda ake korafin rashin amfani da ‘yan wasan gida a tawagar babbar kungiyar kwallon kafa ta Najeriya. Sabanin a baya, da hukumar kwallon kafa ta Najeriyar, kan shirya wasanni na musamman domin fitar da 'yan wasan da za ta yi amfani da su wajen wakiltar kasar a manyan wasanni.Kan wannan kalubale ne Khamis Saleh ya tattauna da masana a fannin kwallon kafa.Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.

página 2 de 2