Wasanni

  • Autor: Vários
  • Narrador: Vários
  • Editor: Podcast
  • Duración: 3:59:28
  • Mas informaciones

Informações:

Sinopsis

A kowace Litinin da Juma'a a shirye-shiryen Safe da Dare ana gabatar da Shirin Duniyar Wasanni akan batutuwa daban-daban da suka shafi wasanni a sassan duniya.

Episodios

  • Yadda wasannin sharen fagen zuwa gasar cin kofin duniya ke gudana a Afrika

    08/09/2025 Duración: 10min

    Kawo yanzu dai wasanni sun ɗauki zafi ganin cewa wasu daga cikin tawagogin ƙasashen sun fara jin kanshin halartar gasar, amma kuma wasu har yanzu tana ƙasa tana dabo. Tawagar ƙasar Morocco tuni ta samu nata tikitin bayan da ta haɗa maki 18, tazarar maki 8 tsakaninta da Tanzania. Tawagogin ƙasashe irinsu Masar da Algeria da Tunisia da Ghana da Afrika ta Kudu, duk da cewa akwai tazarar maki masu ɗan dama tsakaninsu da waɗanda ke mataki na biyu a rukunansu, har yanzu akwai sauran rina a kaba.

  • Yadda ake samun takun saƙa tsakanin ƙungiyoyi da 'yan wasa wajen canza sheƙa

    01/09/2025 Duración: 10min

    Shirin a wannan makon zayyi duba ne kan yadda ake samun takun saƙa tsakanin ƴan wasa da ƙungiyoyinsu a duk lokacin da suke son sauya sheƙa. A duk lokacin da a ka buɗe kasuwar sayen ƴan wasa a duniya, a kan samu takaddama lokaci zuwa lokaci tsakanin ƴan wasa da kuma ƙungiyoyin su saboda wasu ƙungiyoyi na kin amincewa da ƴan wasansu su sauya sheka lokacin da su kuma ƴan wasan ke son bari.

  • Sabon jagorancin ƙungiyar Ranchers Bees na ƙoƙarin farfaɗo da martabarta

    25/08/2025 Duración: 09min

    Shirin Duniyar Wasanni a wannan mako ya yi dubu ne kan amsar ragamar jagorancin ƙungiyar Ranchers Bees da ke jihar Kaduna a Najeriya, da ɗan wasan Super Eagles Sadiq Umar Jololo da kuma ɗan majalisar wakilai Hon. Bello El-Rufai suka yi. Ƙungiyar kwallon ƙafa ta Ranchers Bees na cikin ƙungiyoyin kwallon ƙafa da suka yi suna a baya amma a ka daina jin ɗuriyarta a yan shekarun nan, duk kuwa da cewa har a Nahiyar Afrika baki ɗaya ƙungiyar ta yi fice. A baya dai ƙungiyar ta Ranchers Bees ta lashe kofin yankin Afrika ta yamma wato WAFU sannan a Najeriya kuwa ta lashe kofin kalubale FA cup da dama. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.............. 

  • Yadda wasanni suka gudana bayan fara sabuwar kakar ƙwallon ƙafa a Turai

    18/08/2025 Duración: 10min

    Shirin 'Duniyar Wasanni' a wannan makon ya mayar da hankali ne a kan yadda aka fara sabuwar kakar ƙwallon ƙafa a bana a manyan Lig-Lig na sassan nahiyar Turai. Manyan wasannin dai sun haɗa da na Firimiyar Ingila, La Ligar Spain, da kuma gasar Ligue 1  na ƙasar Faransa. Kamar yadda za a ji cikin shirin tare da Khamis Saleh, Liverpool ce ta fara buɗe sabuwar kakar wasa a Firimiyar Ingila inda ta lallasa Bournemouth da ƙwallaye 4-2.

página 2 de 2